Watchtower LABURARE NA INTANE
Watchtower
LABURARE NA INTANE
Hausa
Ɓ
  • Ā
  • ā
  • Ɓ
  • ɓ
  • ɗ
  • Ɗ
  • Ƙ
  • ƙ
  • ꞌY
  • ꞌy
  • LITTAFI MAI TSARKI
  • WALLAFE-WALLAFE
  • TARO
  • bm sashe na 21 p. 24
  • An Ta da Yesu Daga Matattu!

Babu bidiyo don wannan zabin

Yi hakuri, bidiyon na da dan matsala

  • An Ta da Yesu Daga Matattu!
  • Littafi Mai Tsarki​—Wane Saƙo Ne Ke Cikinsa?
  • Makamantan Littattafai
  • Manzanni Sun Yi Wa’azi da Gaba Gaɗi
    Littafi Mai Tsarki​—Wane Saƙo Ne Ke Cikinsa?
  • Allah Ya Tuna da Dansa
    Ka Koya Daga Wurin Babban Malami
  • Allah Ya Tayar da Yesu Daga Matattu
    Darussa daga Littafi Mai Tsarki
  • Yesu Ya Yi Annabci Mai Girma
    Littafi Mai Tsarki​—Wane Saƙo Ne Ke Cikinsa?
Dubi Ƙari
Littafi Mai Tsarki​—Wane Saƙo Ne Ke Cikinsa?
bm sashe na 21 p. 24

Sashe 21

An Ta da Yesu Daga Matattu!

Yesu ya bayyana ga mabiyansa don ya ba su umurni kuma ya ƙarfafa su

ARANA ta uku bayan mutuwar Yesu, wasu mata waɗanda mabiyansa ne sun ga cewa an kawar da dutsen da aka rufe bakin kabarin da shi. Ban da haka, babu komi a cikin kabarin!

Sai mala’iku biyu suka bayyana. “Kuna neman Yesu, Ba-nazarat,” in ji guda a cikinsu. “Ya tashi.” (Markus 16:6) Ba tare da ɓata lokaci ba, matan suka ruga don su gaya wa manzannin. A kan hanyarsu, sun haɗu da Yesu. “Kada ku ji tsoro,” in ji shi. “Ku tafi, ku faɗa wa ’yan’uwana su tafi zuwa cikin Galili, can kuwa za su gan ni.”—Matta 28:10.

A wannan ranar, mabiyansa su biyu suna tafiya daga Urushalima zuwa ƙauyen Imwasu. Wani baƙo ya haɗu da su kuma ya tambaye su abin da suke tattaunawa. Amma, mutumin Yesu ne da aka ta da daga matattu, wanda ya bayyana a fasalin da ba su gane ba da farko. Da fuskar da ke cike da baƙin ciki sun mai da martani cewa suna tattaunawa ne game da Yesu. Baƙon ya soma bayyana batutuwa game da Almasihu a cikin dukan Nassosi. Hakika, Yesu ya cika dukan annabce-annabcen da aka yi game da Almasihu daga farko har ƙarshe.a Sa’ad da almajiran suka fahimci cewa Yesu ne baƙon, wanda aka ta da daga matattu a matsayin ruhu, sai ya ɓace.

Nan da nan almajiran biyu suka koma Urushalima. A nan suka tarar da manzannin sun taru a cikin wani ɗakin da aka rufe ƙofofin. Yayin da su biyun suke faɗin abin da suka gani, sai Yesu ya bayyana. Abin ya ba mabiyansa mamaki sosai! “Don menene kuwa zacezace suna tashi a cikin zuciyarku?” Yesu ya tambaye su. “Hakanan aka rubuta, Kristi za ya sha wahala, za ya tashi daga matattu kuma kan rana ta uku.”—Luka 24:38, 46.

A cikin kwanaki 40 bayan an ta da shi daga matattu, Yesu ya bayyana ga almajiransa a lokatai dabam-dabam. Akwai lokacin da ya bayyana ga mutane fiye da 500! Wataƙila a wannan lokacin ne ya ba su wannan aikin mai girma: “Ku tafi . . . ku almajirtarda dukan al’ummai, . . . kuna koya musu su kiyaye dukan iyakar abin da na umurce ku: ga shi kuwa ina tare da ku kullayaumi har matuƙar zamani.”—Matta 28:19, 20.

A taronsa na ƙarshe da manzanninsa 11 masu aminci, Yesu ya yi alkawari: “Za ku karɓi iko lokacin da Ruhu Mai-tsarki ya zo bisanku; za ku zama shaiduna . . . har kuma iyakan duniya.” (Ayukan Manzanni 1:8) Bayan haka aka yi sama da Yesu, kuma gajimare ya hana su ganinsa yayin da yake yin sama.

—An ɗauko daga Matta sura ta 28; Markus sura ta 16; Luka sura ta 24; Yohanna surori na 20 da 21; 1 Korintiyawa 15:5, 6.

[Hasiya]

a Don samun misalan annabce-annabce game da Almasihu da suka cika a kan Yesu, ka duba shafuffuka na 17-19 na wannan mujallar da kuma shafuffuka na 199-201 na littafin nan Menene Ainihi Littafi Mai Tsarki Yake Koyarwa?

◼ Ta yaya ne almajiran Yesu suka san cewa Allah ya ta da shi daga matattu?

◼ Menene Yesu ya bayyana wa almajirai biyu da ya haɗu da su a kan hanyar zuwa Imwasu?

◼ Waɗanne umurni ne Yesu ya ba almajiransa kafin ya koma sama?

[Akwati a shafi na 24]

RUHU MAI TSARKI

Ruhu mai tsarki na Allah shi ne iko mafi ƙarfi a sararin samaniya. Jehobah ya yi amfani da ruhunsa, ko ƙarfin iko, ya halicci sama da duniya kuma ya ja-goranci rubuta Littafi Mai Tsarki. Wannan ruhun shi ne ikon da ake yin amfani da shi a dukan mu’ujizan da muka karanta game da su, har da mafi girma a cikin su, wato, ta da Yesu Kristi daga matattu zuwa rai a matsayin ruhu mai iko sosai.—Farawa 1:2; 2 Samuila 23:2; Ayukan Manzanni 10:38; 1 Bitrus 3:18.

[Taswira a shafi na 24]

Farawa

Fitowa

Levitikus

Littafin Lissafi

Kubawar Shari’a

Joshua

Alƙalawa

Ruth

1 Sama’ila

2 Sama’ila

1 Sarakuna

2 Sarakuna

1 Labarbaru

2 Labarbaru

Ezra

Nehemiya

Esther

Ayuba

Zabura

Misalai

Mai-Wa’azi

Waƙar Waƙoƙi

Ishaya

Irmiya

Makoki

Ezekiel

Daniyel

Hosiya

Joel

Amos

Obadiya

Yunana

Mikah

Nahum

Habakkuk

Zafaniya

Haggai

Zakariya

Malakai

● Matta

● Markus

● Luka

● Yohanna

Ayyukan Manzanni

Romawa

1 Korintiyawa

2 Korintiyawa

Galatiyawa

Afisawa

Filibiyawa

Kolosiyawa

1 Tasalonikawa

2 Tasalonikawa

1 Timotawus

    Littattafan Hausa (1987-2026)
    Fita
    Shiga Ciki
    • Hausa
    • Raba
    • Wadda ka fi so
    • Copyright © 2025 Watch Tower Bible and Tract Society of Pennsylvania
    • Ka'idojin Amfani
    • Tsarin Tsare Sirri
    • Saitin Tsare Sirri
    • JW.ORG
    • Shiga Ciki
    Raba