Watchtower LABURARE NA INTANE
Watchtower
LABURARE NA INTANE
Hausa
Ɓ
  • Ā
  • ā
  • Ɓ
  • ɓ
  • ɗ
  • Ɗ
  • Ƙ
  • ƙ
  • ꞌY
  • ꞌy
  • LITTAFI MAI TSARKI
  • WALLAFE-WALLAFE
  • TARO
  • w15 7/1 p. 16
  • Amsoshin Tambayoyi Daga Littafi Mai Tsarki

Babu bidiyo don wannan zabin

Yi hakuri, bidiyon na da dan matsala

  • Amsoshin Tambayoyi Daga Littafi Mai Tsarki
  • Hasumiyar Tsaro Mai Shelar Mulkin Jehobah—2015
  • Makamantan Littattafai
  • Mene Ne Zai Faru a Ranar Shari’a?
    Hasumiyar Tsaro Mai Shelar Mulkin Jehobah—2012
  • Mecece Ranar Shari’a?
    Menene Ainihi Littafi Mai Tsarki Yake Koyarwa?
Hasumiyar Tsaro Mai Shelar Mulkin Jehobah—2015
w15 7/1 p. 16

AMSOSHIN TAMBAYOYI DAGA LITTAFI MAI TSARKI

Mece ce Ranar Shari’a?

Wata iyali sun tashi daga mutuwa a lokacin sarautar Yesu ta shekara dubu kuma suna farin ciki

Ma Ya Sa Ranar Shari’a Za Ta Zama Ranar Farin Ciki?

A zamanin dā, Allah ya yi amfani da alƙalai don ya cece mutanensa daga masu zalunci. (Alƙalawa 2:18) Littafi Mai Tsarki ya ce Ranar Shari’a za ta zama lokacin farin ciki domin Jehobah wanda shi ne alƙalin dukan duniya zai ceci ’yan Adam daga masu zalunci.—Karanta Zabura 96:12, 13; Ishaya 26:9.

Allah ya naɗa Yesu don ya shari’anta masu rai da kuma matattu. (Ayyukan Manzanni 10:42; 17:31) Mutane da yawa sun mutu ba tare da sanin Allah ba. Saboda haka, a Ranar Shari’a, Yesu zai ta da waɗannan mutanen domin a koya musu game da Allah na gaskiya kuma su ƙaunace shi.—Karanta Ayyukan Manzanni 24:15.

Me ya sa Ranar Shari’a za ta ɗauki tsawon shekaru dubu?

Za a ta da matattu a lokacin sarautar Yesu ta shekaru dubu. (Ru’ya ta Yohanna 20:4, 12) Za su bukaci lokaci don su koya game da Jehobah kuma su yi masa biyayya. Akasin ra’ayoyin mutane, Littafi Mai Tsarki ya ce za a shari’anta mutane bisa ga abubuwan da suka yi bayan da aka ta da su daga mutuwa.—Karanta Romawa 6:7.

Littafi Mai Tsarki ya ce ranar shari’a za ta zo farat ɗaya, kafin shekaru dubun su soma. An kuma kira wannan ranar ƙarshe, kamar yadda aka tattauna a talifofi na farko na wannan mujallar. A wannan ranar, Allah zai halaka dukan miyagun mutane. (2 Bitrus 3:7) Saboda haka, ya kamata mu nuna cewa muna ƙaunar Allah.—Karanta 2 Bitrus 3:9, 13.

Don ƙarin bayani, ka duba shafi na 213 a wannan littafin, Shaidun Jehobah ne suka wallafa

Za ka kuma iya samunsa a dandalin www.pr418.com/ha

    Littattafan Hausa (1987-2026)
    Fita
    Shiga Ciki
    • Hausa
    • Raba
    • Wadda ka fi so
    • Copyright © 2025 Watch Tower Bible and Tract Society of Pennsylvania
    • Ka'idojin Amfani
    • Tsarin Tsare Sirri
    • Saitin Tsare Sirri
    • JW.ORG
    • Shiga Ciki
    Raba