Watchtower LABURARE NA INTANE
Watchtower
LABURARE NA INTANE
Hausa
Ɓ
  • Ā
  • ā
  • Ɓ
  • ɓ
  • ɗ
  • Ɗ
  • Ƙ
  • ƙ
  • ꞌY
  • ꞌy
  • LITTAFI MAI TSARKI
  • WALLAFE-WALLAFE
  • TARO
  • ijwbq talifi na 127
  • A Ina ne Kayinu Ya Sami Matarsa?

Babu bidiyo don wannan zabin

Yi hakuri, bidiyon na da dan matsala

  • A Ina ne Kayinu Ya Sami Matarsa?
  • Amsoshin Tambayoyi Daga Littafi Mai Tsarki
  • Ƙananan Jigo
  • Makamantan Littattafai
  • Amsar Littafi Mai Tsarki
  • Fushi Ya Jawo Kisan Kai
    Darussa daga Littafi Mai Tsarki
  • Ɗan Kirki, Da Kuma Mugun Ɗa
    Littafina na Labarun Littafi Mai Tsarki
  • Su Waye Ne ’Yan’uwanmu?
    Ka Koya Daga Wurin Babban Malami
Amsoshin Tambayoyi Daga Littafi Mai Tsarki
ijwbq talifi na 127
Kayinu da matarsa

A Ina ne Kayinu Ya Sami Matarsa?

Amsar Littafi Mai Tsarki

Dan farin iyayenmu na farko, wato Kayinu ya auri daya daga cikin kannensa mata ko kuma danginsa. Mun fahimci hakan ne ta wurin bincika abin da Littafi Mai Tsarki ya fada game da Kayinu da kuma danginsa.

Gaskiya game da Kayinu da kuma danginsa

  • Dukan ‘yan Adam ‘ya’yan Adamu da Hawwa’u ne. Allah “ya halicci dukan al’umma daga mutum guda [Adamu], domin su zauna a dukan fuskar duniya.” (Ayyukan Manzanni 17:​26, Juyi Mai Fitar da Ma’ana) Matar Adamu, wato Hawwa’u ita ce “uwar masu rai duka.” (Farawa 3:20) Saboda haka, Kayinu ya auri daya daga cikin kannensa.

  • Kayinu da dan’uwansa Habila suna cikin yaran farko da Hawwa’u ta haifa. (Farawa 4:​1, 2) A lokacin da aka kori Kayinu don ya kashe dan’uwansa, Kayinu ya ce, duk “wanda ya same ni za ya kashe ni.” (Farawa 4:14) Su waye ne Kayinu ya ji tsoronsu? Littafi Mai Tsarki ya ce Adamu ‘ya kuma haifi ‘ya’ya maza da mata.’ (Farawa 5:4) Da alama wasu yaran Adamu da Hawwa’u sun sa Kayinu a gaba shi ya sa yake tsoronsu.

  • A dā, mutane suna iya auran danginsu. Alal misali, Ibrahim ya auri ‘yar matar babansa. (Farawa 20:12) Amma an fara haramta irin wannan auren a lokacin da aka ba da Doka ta hannun Musa kuma hakan ya faru ne shekaru da yawa bayan zamanin Kayinu. (Levitikus 18:​9, 12, 13) Da alama a lokacin idan mutum ya auri ‘yar’uwarsa kuma suka haihu, yaran ba sa samun lahani kamar yadda ake gani a yanzu.

  • Littafi Mai Tsarki ya ba da labarin Adamu da Hawwa’u da iyalinsa daidai yadda ya faru. Ba littafin Farawa da Musa ya rubuta ba ne kawai ya ba da labarin zuriyar Adamu dalla-dalla, wasu ‘yan tarihi ma kamar su Ezra da Luka sun yi hakan. (Farawa 5:​3-5; 1 Labarbaru 1:​1-4; Luka 3:38) Marubutan Littafi Mai Tsarki ma sun ambaci labarin Kayinu a matsayin abin da ya faru a dā.​—Ibraniyawa 11:4; 1 Yohanna 3:12; Yahuda 11.

    Littattafan Hausa (1987-2026)
    Fita
    Shiga Ciki
    • Hausa
    • Raba
    • Wadda ka fi so
    • Copyright © 2025 Watch Tower Bible and Tract Society of Pennsylvania
    • Ka'idojin Amfani
    • Tsarin Tsare Sirri
    • Saitin Tsare Sirri
    • JW.ORG
    • Shiga Ciki
    Raba