Ƙarin Bayani
a Da yake magana a kan zancen Bulus cewa “ƙauna tana da yawan haƙuri,” manazarin Littafi Mai Tsarki Gordon D. Fee ya rubuta: “A cikin koyarwar Bulus [tsawon jimrewa da alheri] suna wakiltar gefe biyu na halin Allah wajen bil Adam (Gwada da Rom. 2:4). A wata sassa, ƙaunar Allah ta jimiri tana bayyana ta wurin riƙe fushinsa wajen tawayen bil Adam ne; a wata sassa kuma, ana ganin alherinsa cikin nuna jinƙai nasa mai yawa. Saboda haka, kwatancin Bulus na ƙauna ya soma da kwatanci kashi biyu game da Allah, wanda ta wurin Kristi ya nuna kansa mai jimiri mai alheri ga waɗanda suka cancanci hukuncinsa.”