Ƙarin Bayani
a Abu mai daraja a dabbar hadaya ita ce jininta, domin abu ne mai daraja a gaban Allah. (Levitikus 17:11) Hakan yana nufin cewa garin da talaka zai ba da bai da daraja ne? A’a. Jehobah ya ɗauki halinsu na tawali’u da kuma yardar rai da suke nuna wajen ba da waɗannan hadayun da tamani. Bugu da ƙari, ana gafarta zunuban dukan al’ummar, har da na talakawa, bisa hadayar da ake yi wa Allah a Ranar Kafara.—Leviticus 16:29, 30.