Ƙarin Bayani
a “Waɗansu tumaki” na Yesu ba za su zama ’ya’yan Allah ba sai ƙarshen shekara dubu. Amma, tun da yake sun keɓe kansu ga Allah, suna iya kiran Allah “Uba” kuma za a iya ɗaukansu a matsayin waɗanda suke cikin iyalin masu bauta na Jehobah.—Yoh. 10:16; Isha. 64:8; Mat. 6:9; R. Yoh. 20:5.