Ƙarin Bayani
b A wasu lokuta, dattawa za su bukaci su yi shari’a idan wani ya yi zunubi mai tsanani ko kuma ya tuba. (1 Kor. 5:11; 6:5; Yak. 5:14, 15) Amma ya kamata su tuna cewa ba za su iya sanin abin da ke zuciyar mutumin ba, kuma shari’ar da suke yi ta Jehobah ce. (Ka duba misalin da ke 2 Tarihi 19:6.) Zai dace su yi koyi da Jehobah ta wajen nuna sanin ya kamata da jinƙai da kuma adalci.