Ƙarin Bayani
a Wannan talifin ya bayyana ƙarin haske da aka samu game da abin da Yesu ya faɗa a Yohanna 5:28, 29 a kan waɗanda za a tā da su su yi rayuwa da waɗanda za a tā da su a yi musu hukunci. Za mu koyi game da abin da tashin matattu guda biyun nan suke nufi da kuma waɗanda za a tā da su a waɗannan tashin matattun.