Ƙarin Bayani
a Wani littafi da ya yi bayani a kan wannan labarin ya ce: “Da alama cewa Yusufu [maigidan Maryamu] ya riga ya rasu da dadewa kuma danta Yesu ne yake kula da ita. Yanzu da za a kashe shi, wa zai kula da ita? . . . Abin da Yesu ya yi a nan, ya koya wa yara cewa ya kamata su dinga kula da iyayensu da suka tsufa.”—The NIV Matthew Henry Commentary in One Volume, shafuffuka na 428-429.