Watchtower LABURARE NA INTANE
Watchtower
LABURARE NA INTANE
Hausa
Ɓ
  • Ā
  • ā
  • Ɓ
  • ɓ
  • ɗ
  • Ɗ
  • Ƙ
  • ƙ
  • ꞌY
  • ꞌy
  • LITTAFI MAI TSARKI
  • WALLAFE-WALLAFE
  • TARO
  • my labari na 5
  • An Fara Rayuwa Mai Wuya

Babu bidiyo don wannan zabin

Yi hakuri, bidiyon na da dan matsala

  • An Fara Rayuwa Mai Wuya
  • Littafina na Labarun Littafi Mai Tsarki
  • Makamantan Littattafai
  • Abin Da Ya Sa Suka Yi Rashin Gidansu
    Littafina na Labarun Littafi Mai Tsarki
  • Yaya Rayuwa Take a Lambun Adnin?
    Ka Saurari Allah Don Ka Rayu Har Abada
  • Adamu da Hauwa’u Sun Ki Bin Dokar Allah
    Darussa daga Littafi Mai Tsarki
  • Allah Ya Yi Mace da Miji na Farko
    Darussa daga Littafi Mai Tsarki
Dubi Ƙari
Littafina na Labarun Littafi Mai Tsarki
my labari na 5

LABARI NA 5

An Fara Rayuwa Mai Wuya

ADAMU da Hauwa’u sun sha wuya ƙwarai bayan da suka fita daga cikin lambun Adnin. Sai sun wahala wajen aiki suke samun abinci. Maimakon itatuwa kyawawa masu ’ya’ya, suka ga ƙayayuwa da sarƙaƙiya suka yi ta tsiro musu. Abin da ya faru ke nan sa’ad da Adamu da Hauwa’u suka yi rashin biyayya ga Allah suka ɓata abokantakar su da shi.

Mafi muni ma, Adamu da Hauwa’u suka fara mutuwa. Ka tuna Allah ya yi musu gargaɗi cewa za su mutu idan suka ci wani ’ya’yan itace. Hakika, a ranar da suka ci suka fara mutuwa. Sun yi wauta ƙwarai da suka ƙi yi wa Allah biyayya!

Adamu da Hauwa’u sun haifi dukan ’ya’yansu ne bayan Allah ya kore su daga lambun Adnin. Wannan yana nufin cewa ’ya’yansu ma za su tsufa kuma su mutu.

Da a ce Adamu da Hauwa’u sun yi wa Jehobah biyayya, da rayuwa ta kasance da daɗi ga su da ’ya’yansu. Da za su zauna har abada cikin jin daɗi a duniya. Da babu wanda zai tsufa, ko ya yi ciwo, ko ya mutu.

Allah yana son mutane su dawwama cikin farin ciki, kuma ya yi alkawarin cewa wata rana hakan zai faru. Dukan duniya za ta yi kyau kuma dukan mutane za su kasance da koshin lafiya. Kuma dukan mutane da suke duniya za su zama abokan juna kuma abokan Allah.

Amma Hauwa’u ba abokiyar Allah ba ce kuma. Saboda haka sa’ad da ta haifi ’ya’yanta ta sha wuya ƙwarai. Ta sha naƙuda. Rashin biyayya ga Jehobah ya jawo mata baƙin ciki ƙwarai, ko ba haka ba ne?

Adamu da Hauwa’u sun haifi ’ya’ya maza da mata da yawa. Sa’ad da suka haifi ɗansu na fari, suka saka masa suna Kayinu. Suka saka wa na biyun suna Habila.Menene ya same su? Ka san abin da ya same su?

Farawa 3:16-23; 4:1, 2; Ru’ya ta Yohanna 21:3, 4.

Tambayoyi na Nazari

    Littattafan Hausa (1987-2026)
    Fita
    Shiga Ciki
    • Hausa
    • Raba
    • Wadda ka fi so
    • Copyright © 2025 Watch Tower Bible and Tract Society of Pennsylvania
    • Ka'idojin Amfani
    • Tsarin Tsare Sirri
    • Saitin Tsare Sirri
    • JW.ORG
    • Shiga Ciki
    Raba