Watchtower LABURARE NA INTANE
Watchtower
LABURARE NA INTANE
Hausa
Ɓ
  • Ā
  • ā
  • Ɓ
  • ɓ
  • ɗ
  • Ɗ
  • Ƙ
  • ƙ
  • ꞌY
  • ꞌy
  • LITTAFI MAI TSARKI
  • WALLAFE-WALLAFE
  • TARO
  • my labari na 31
  • Musa Da Haruna Sun Je Wurin Fir’auna

Babu bidiyo don wannan zabin

Yi hakuri, bidiyon na da dan matsala

  • Musa Da Haruna Sun Je Wurin Fir’auna
  • Littafina na Labarun Littafi Mai Tsarki
  • Makamantan Littattafai
  • Annoba ta Daya Zuwa Uku
    Darussa daga Littafi Mai Tsarki
  • Annoba ta Hudu Zuwa Tara
    Darussa daga Littafi Mai Tsarki
  • Allah Ya Ceci ’Ya’yan Isra’ila
    Littafi Mai Tsarki​—Wane Saƙo Ne Ke Cikinsa?
  • Musa Ya Bauta wa Jehobah
    Darussa daga Littafi Mai Tsarki
Dubi Ƙari
Littafina na Labarun Littafi Mai Tsarki
my labari na 31

LABARI NA 31

Musa Da Haruna Sun Je Wurin Fir’auna

SA’AD da Musa ya koma ƙasar Masar, ya gaya wa wansa Haruna game da mu’ujizar. Sa’ad da Musa da Haruna suka nuna wa Isra’ilawa dukan waɗannan mu’ujizar, mutanen suka yarda cewa Jehobah yana tare da su.

Sai Musa da Haruna suka je wurin Fir’auna. Suka gaya masa: ‘Jehobah Allah na Isra’ila ya ce, “Ka ƙyale mutane na na kwana uku, saboda su bauta mini a cikin daji.”’ Amma Fir’auna ya amsa: ‘Ni ban yarda da Jehobah ba. Kuma ba zan ƙyale Isra’ilawa su tafi ba.’

Fir’auna ya fusata, domin mutanen suna neman hutu daga aiki domin su bauta wa Jehobah. Saboda haka ya tilasta musu su yi aiki ma fiye da dā. Isra’ilawa suka ga laifin Musa domin yadda ake gana musu azaba, kuma Musa bai yi farin ciki ba. Amma Jehobah ya gaya masa cewa kada ya damu. ‘Zan sa Fir’auna ya ƙyale mutane na,’ in ji Jehobah.

Musa da Haruna suka sake komawa wurin Fir’auna. A wannan lokacin suka yi mu’ujiza. Haruna ya jefar da sandansa sai ya zama babban maciji. Amma masu hikimar Fir’auna ma suka jefar da sandunan su suka zama macizai. Amma ka gani! Macijin Haruna yana cinye na masu hikiman. Duk da haka Fir’auna ya ƙi ƙyale Isra’ilawa su tafi.

Sai lokaci ya yi da Jehobah zai koya wa Fir’auna hankali. Ka san yadda ya yi haka? Ta wurin kawo annoba 10, ko kuma manyan masifu bisa ƙasar Masar.

Bayan kowane annoba, sai Fir’auna ya sa a kira Musa, ya ce: ‘Ka dakatar da annobar, zan ƙyale Isra’ilawa su tafi.’ Amma bayan annobar ta ƙare, sai Fir’auna ya ƙi. Ya ƙi ƙyale Isra’ilawa su tafi. Amma a ƙarshe, bayan annoba ta 10, Fir’auna ya ƙyale Isra’ilawa suka tafi.

Ka san dukan annoba 10? Ka juya zuwa shafi na gaba bari mu koya game da su.

Fitowa 4:27-31; 5:1-23; 6:1-13, 26-30; 7:1-13.

Tambayoyi na Nazari

    Littattafan Hausa (1987-2026)
    Fita
    Shiga Ciki
    • Hausa
    • Raba
    • Wadda ka fi so
    • Copyright © 2025 Watch Tower Bible and Tract Society of Pennsylvania
    • Ka'idojin Amfani
    • Tsarin Tsare Sirri
    • Saitin Tsare Sirri
    • JW.ORG
    • Shiga Ciki
    Raba