Watchtower LABURARE NA INTANE
Watchtower
LABURARE NA INTANE
Hausa
Ɓ
  • Ā
  • ā
  • Ɓ
  • ɓ
  • ɗ
  • Ɗ
  • Ƙ
  • ƙ
  • ꞌY
  • ꞌy
  • LITTAFI MAI TSARKI
  • WALLAFE-WALLAFE
  • TARO
  • bm sashe na 2 p. 5
  • Aljannar da Aka Rasa

Babu bidiyo don wannan zabin

Yi hakuri, bidiyon na da dan matsala

  • Aljannar da Aka Rasa
  • Littafi Mai Tsarki​—Wane Saƙo Ne Ke Cikinsa?
  • Makamantan Littattafai
  • Yaya Rayuwa Take a Lambun Adnin?
    Ka Saurari Allah Don Ka Rayu Har Abada
  • Wasu Sun Fi Mu Matsayi
    Ka Koya Daga Wurin Babban Malami
  • Adamu da Hauwa’u Sun Ki Bin Dokar Allah
    Darussa daga Littafi Mai Tsarki
  • An Fara Rayuwa Mai Wuya
    Littafina na Labarun Littafi Mai Tsarki
Dubi Ƙari
Littafi Mai Tsarki​—Wane Saƙo Ne Ke Cikinsa?
bm sashe na 2 p. 5

Sashe 2

Aljannar da Aka Rasa

Wani mala’ika ɗan tawaye ya rinjayi mace da namiji na farko, Adamu da Hauwa’u su ƙi sarautar Allah. A sakamakon haka, zunubi da mutuwa suka addabi ’yan adam

TUN da daɗewa kafin a halicci mutane, Allah ya halicci halittun ruhohi masu yawa, wato, mala’iku. A lambun Adnin, wani mala’ika ɗan tawaye, wanda ya zama Shaiɗan Iblis, ya jarraba Hauwa’u cikin dabara don ta ci ’ya’yan itacen da Allah ya hana.

Ta wajen yin magana ta hanyar maciji, Shaiɗan ya faɗi cewa Allah yana hana matar da mijinta wani abu mai kyau. Mala’ikan ya gaya wa Hauwa’u cewa ita da mijinta ba za su mutu ba idan suka ci ’ya’yan itacen da aka hana. Da haka, Shaiɗan ya zargi Allah cewa Yana yi wa ’ya’yansa ’yan adam ƙarya. Mai Ruɗin ya gabatar da rashin biyayya ga Allah a matsayin tafarki mai kyau da zai kai ga wayewa da kuma ’yanci. Amma, hakan ƙarya ne, kuma shi ne ƙarya na farko da aka fara yi a duniya. Ainihin batun da hakan ya ƙunsa shi ne ikon mallaka na Allah, ko kuwa yin sarautar dukan duniya, wato, ko Allah yana da ikon yin sarauta da kuma ko yana amfani da ikonsa cikin adalci don talakawansa su amfana sosai.

Hauwa’u ta yarda da ƙaryar da Shaiɗan ya yi. Ta soma sha’awar ’ya’yan itacen, kuma daga baya ta ci daga ciki. Bayan haka, ta ba mijinta, kuma ya ci. Da haka, suka zama masu zunubi. Wannan abin da suka yi alama ce na tawaye. Ta wajen yin rashin biyayya ga dokar Allah da gangan, Adamu da Hauwa’u sun ƙi sarautar Mahalicci wanda ya ba su komi, har da kamiltaccen rai.

Allah ya yi wa ’yan tawayen hukunci domin abubuwan da suka aikata. Ya annabta zuwan Iri da aka alkawarinsa, ko Mai Ceto, wanda zai halaka Shaiɗan, da maciji ya wakilta. Allah bai halaka Adamu da Hauwa’u nan da nan ba, ta hakan, ya nuna tausayi ga yaran da ba su haifa ba. Waɗannan yaran za su kasance da bege domin Wanda Allah zai aiko zai kawar da sakamako marar kyau da ya samo asali daga Adnin. Yayin da aka ci gaba da rubuta Littafi Mai Tsarki, an bayyana a hankali yadda za a cika nufin Allah game da Mai Ceto da zai zo a nan gaba da kuma Wanda za a aiko.

Allah ya kori Adamu da Hauwa’u daga Aljannar. Za su yi aiki tuƙuru da jiɓi don su tallafa wa kansu ta wajen yin shuka a waje da lambun Adnin. Bayan haka, Hauwa’u ta yi ciki kuma ta haifi Kayinu, wanda shi ne ɗan fari na Adamu da Hauwa’u. Ma’auratan sun haifi yara maza da mata, har da Habila da Shitu, kakan-kakan Nuhu.

—An ɗauko daga Farawa surori 3 zuwa 5; Ru’ya ta Yohanna 12:9.

◼ Wace ƙarya ce ta farko, kuma wanene ya yi ta?

◼ Ta yaya ne Adamu da Hauwa’u suka yi hasarar Aljanna?

◼ Sa’ad da yake yi wa ’yan tawayen hukunci domin abubuwan da suka aikata, wane bege ne Allah ya yi tanadinsa?

[Bayanin da ke shafi na 5]

Zuriyar “za ya ƙuje kanka, kai kuma za ka ƙuje duddugensa.”​—Farawa 3:15

[Akwati a shafi na 5]

AJIZANCI DA MUTUWA

Allah ya halicci Adamu da Hauwa’u a matsayin kamiltattu, da begen cewa za su rayu har abada a Aljanna. Sun yi zunubi sa’ad da suka yi tawaye ga Allah. Da haka, Adamu da Hauwa’u suka zama ajizai kuma suka ɓata dangantakarsu da Tushen rai, Jehobah. Tun daga wannan lokacin, su da dukan zuriyarsu ajizai sun kasa guje wa zunubi da mutuwa.—Romawa 5:12.

[Taswira a shafi na 5]

Farawa ●

Fitowa

Levitikus

Littafin Lissafi

Kubawar Shari’a

Joshua

Alƙalawa

Ruth

1 Sama’ila

2 Sama’ila

1 Sarakuna

2 Sarakuna

1 Labarbaru

2 Labarbaru

Ezra

Nehemiya

Esther

Ayuba

Zabura

Misalai

Mai-Wa’azi

Waƙar Waƙoƙi

Ishaya

Irmiya

Makoki

Ezekiel

Daniyel

Hosiya

Malakai

Matta

Markus

Luka

Yohanna

Ayyukan Manzanni

Romawa

1 Korintiyawa

2 Korintiyawa

Galatiyawa

Afisawa

Filibiyawa

Kolosiyawa

1 Tasalonikawa

2 Tasalonikawa

1 Timotawus

2 Timotawus

Titus

Filimon

Ibraniyawa

Yaƙub

1 Bitrus

2 Bitrus

1 Yohanna

2 Yohanna

3 Yohanna

Wasiƙa ta Yahuda

Ru’ya ta Yohanna

    Littattafan Hausa (1987-2026)
    Fita
    Shiga Ciki
    • Hausa
    • Raba
    • Wadda ka fi so
    • Copyright © 2025 Watch Tower Bible and Tract Society of Pennsylvania
    • Ka'idojin Amfani
    • Tsarin Tsare Sirri
    • Saitin Tsare Sirri
    • JW.ORG
    • Shiga Ciki
    Raba