Watchtower LABURARE NA INTANE
Watchtower
LABURARE NA INTANE
Hausa
Ɓ
  • Ā
  • ā
  • Ɓ
  • ɓ
  • ɗ
  • Ɗ
  • Ƙ
  • ƙ
  • ꞌY
  • ꞌy
  • LITTAFI MAI TSARKI
  • WALLAFE-WALLAFE
  • TARO
  • bm sashe na 4 p. 7
  • Allah Ya Ɗauki Alkawari da Ibrahim

Babu bidiyo don wannan zabin

Yi hakuri, bidiyon na da dan matsala

  • Allah Ya Ɗauki Alkawari da Ibrahim
  • Littafi Mai Tsarki​—Wane Saƙo Ne Ke Cikinsa?
  • Makamantan Littattafai
  • Jehobah Ya Kira Shi “Aminina”
    Hasumiyar Tsaro Mai Shelar Mulkin Jehobah (Na Nazari)—2016
  • Ibrahim da Saratu Sun Yi Biyayya ga Allah
    Darussa daga Littafi Mai Tsarki
  • Allah Ya Gwada Bangaskiyar Ibrahim
    Littafina na Labarun Littafi Mai Tsarki
  • Kana Jiran “Birnin Nan Wanda Yake da Tushe”?
    Hasumiyar Tsaro Mai Shelar Mulkin Jehobah (Na Nazari)—2020
Dubi Ƙari
Littafi Mai Tsarki​—Wane Saƙo Ne Ke Cikinsa?
bm sashe na 4 p. 7

Sashe 4

Allah Ya Ɗauki Alkawari da Ibrahim

Ibrahim ya yi biyayya ga Allah cike da bangaskiya, kuma Jehobah ya yi alkawari cewa zai albarkace shi kuma zai ƙara yawan zuriyoyinsa

SHEKARU wajen 350 sun riga sun wuce da aukuwar Rigyawa ta zamanin Nuhu. Ibrahim uban iyali yana zaune a birni mai arziki a Ur, wato, inda ƙasar Iraƙi ta zamani ta ke. Ibrahim mutumi ne mai bangaskiya sosai. Amma a yanzu ana son a jarraba bangaskiyarsa.

Jehobah ya gaya wa Ibrahim ya bar ƙasar da aka haife shi kuma ya koma wata ƙasa, wato, Ka’anan. Ibrahim ya yi biyayya ba tare da yin ja-in-ja ba. Ya tafi da iyalinsa, har da matarsa, Saratu, da ɗan’uwansa Lutu, kuma bayan wannan tafiyar mai nisa, ya zama mai zama a cikin tanti a Ka’anan. A cikin alkawarin da Ya yi da Ibrahim, Jehobah ya yi alkawarin cewa zai fito da wata al’umma mai girma daga cikinsa, za a yi wa dukan iyalan da ke duniya albarka ta hanyarsa, kuma ’ya’yansa za su gaji ƙasar Ka’anan.

Ibrahim da Lutu sun yi arziki, sun tara garken tumaki da shanu masu yawa. Ba tare da nuna son kai ba, Ibrahim ya ƙyale Lutu ya zaɓi yankin da yake so. Lutu ya zaɓi ƙasar da ke da ni’ima da ke yankin Kogin Urdun kuma ya zauna a birnin Saduma. Mutanen Saduma ’yan iska ne, suna mugun zunubi ga Jehobah.

Daga baya, Jehobah Allah ya tabbatar wa Ibrahim cewa zuriyarsa za ta yi yawa kamar taurarin sama. Ibrahim ya yi imani da wannan alkawarin. Duk da haka, Saratu, ƙaunatacciyar matar Ibrahim, ba ta haihu ba. Sa’ad da Ibrahim ya kai ɗan shekara casa’in da tara kuma Saratu ta kai wajen shekara casa’in, Allah ya gaya wa Ibrahim cewa shi da Saratu za su haifi ɗa. Kamar yadda Allah ya faɗa, Saratu ta haifi Ishaku. Ibrahim yana da yara, amma Mai Ceto da aka yi alkawarinsa a Adnin zai zo ne ta hanyar Ishaku.

Shi kuwa Lutu da iyalinsa suna zaune a Saduma, amma Lutu mai aminci bai bi halin lalatattu mazauna birnin ba. Sa’ad da Jehobah ya yanke shawarar hukunta Saduma, ya aika mala’iku don su je su gaya wa Lutu halakar da ke tafe. Mala’ikun sun umurci Lutu da iyalinsa su gudu daga Saduma kuma kada su kalli baya. Bayan haka, Allah ya yi ruwan wuta da ƙibiritu a kan Saduma da kuma mugun birnin da ke kusa da ita, Gwamrata, kuma ya halaka dukan mazauna cikinsu. Lutu da ’ya’yansa biyu mata sun tsira. Amma matar Lutu ta kalli baya, wataƙila don marmarin abubuwan da ta bari. Ta rasa ranta domin wannan rashin biyayyar.

—An ɗauko daga Farawa 11:10–19:38.

◼ Me ya sa Ibrahim ya koma Ka’anan?

◼ Wane alkawari ne Jehobah ya yi da Ibrahim?

◼ Me ya sa Jehobah ya halaka Saduma da Gwamrata?

[Akwati a shafi na 7]

ALLAHN ALKAWURA

A zamanin da aka rubuta Littafi Mai Tsarki, alkawari yarjejeniya ce. Ta hanyar jerin alkawuran da Ya yi, da sannu-sannu Jehobah ya bayyana yadda manufarsa game da Mai Ceto da aka yi alkawarinsa a Adnin zai cika. Alkawarin da ya yi da Ibrahim ya nuna cewa Wanda aka yi alkawarinsa zai fito ne daga zuriyar Ibrahim. Alkawuran da aka yi daga baya za su ba da ƙarin haske wajen gane Wanda aka yi alkawarinsa.

[Taswira a shafi na 7]

Farawa ●

Fitowa

Levitikus

Littafin Lissafi

Kubawar Shari’a

Joshua

Alƙalawa

Ruth

1 Sama’ila

2 Sama’ila

1 Sarakuna

2 Sarakuna

1 Labarbaru

2 Labarbaru

Ezra

Nehemiya

Esther

Ayuba

Zabura

Misalai

Mai-Wa’azi

Waƙar Waƙoƙi

Ishaya

Irmiya

Makoki

Ezekiel

Daniyel

Hosiya

Joel

Amos

Obadiya

Yunana

Mikah

Nahum

Habakkuk

Zafaniya

Haggai

Zakariya

Malakai

Matta

Markus

Luka

Yohanna

Ayyukan Manzanni

Romawa

1 Korintiyawa

2 Korintiyawa

Galatiyawa

Afisawa

Filibiyawa

Kolosiyawa

1 Tasalonikawa

2 Tasalonikawa

1 Timotawus

2 Timotawus

Titus

Filimon

Ibraniyawa

Yaƙub

1 Bitrus

2 Bitrus

1 Yohanna

2 Yohanna

3 Yohanna

Wasiƙa ta Yahuda

Ru’ya ta Yohanna

    Littattafan Hausa (1987-2026)
    Fita
    Shiga Ciki
    • Hausa
    • Raba
    • Wadda ka fi so
    • Copyright © 2025 Watch Tower Bible and Tract Society of Pennsylvania
    • Ka'idojin Amfani
    • Tsarin Tsare Sirri
    • Saitin Tsare Sirri
    • JW.ORG
    • Shiga Ciki
    Raba