Watchtower LABURARE NA INTANE
Watchtower
LABURARE NA INTANE
Hausa
Ɓ
  • Ā
  • ā
  • Ɓ
  • ɓ
  • ɗ
  • Ɗ
  • Ƙ
  • ƙ
  • ꞌY
  • ꞌy
  • LITTAFI MAI TSARKI
  • WALLAFE-WALLAFE
  • TARO
  • lfb darasi na 45 p. 110-p. 111 par. 2
  • An Raba Mulkin

Babu bidiyo don wannan zabin

Yi hakuri, bidiyon na da dan matsala

  • An Raba Mulkin
  • Darussa daga Littafi Mai Tsarki
  • Makamantan Littattafai
  • An Raba Mulkin
    Littafina na Labarun Littafi Mai Tsarki
  • Jehobah Ba Zai Yashe Amintattunsa Ba
    Hasumiyar Tsaro Mai Shelar Mulkin Jehobah—2008
  • Da Ya Sami Tagomashin Allah
    Hasumiyar Tsaro Mai Shelar Mulkin Jehobah (Na Nazari)—2018
  • Darussa Daga Littafin Sarakuna na Ɗaya
    Hasumiyar Tsaro Mai Shelar Mulkin Jehobah—2005
Darussa daga Littafi Mai Tsarki
lfb darasi na 45 p. 110-p. 111 par. 2
Sai Ahaija ya yayyaga rigarsa waje 12 a gaban Jeroboam

DARASI NA 45

An Raba Mulkin

Sa’ad da Sulemanu yake bauta wa Jehobah, akwai salama sosai a Isra’ila. Amma daga baya, sai ya auri mata da yawa masu bautar gumaka daga wasu ƙasashe. A hankali, a hankali, sai Sulemanu ya soma bauta wa gumaka. Hakan ya sa Jehobah fushi. Sai ya ce wa Sulemanu: ‘Zan ƙwace mulkin daga hannunka kuma in raba shi biyu. Zan ba da mafi girma ga bawanka kuma iyalinka za ta ɗauki wanda ya fi ƙarami.’

Jehobah ya yi amfani da wata hanya don ya sanar da nufinsa. Akwai wata rana da wani bawan Sulemanu mai suna Jeroboam yake tafiya, sai ya haɗu da annabi Ahaija. Sai Ahaija ya yayyaga rigarsa waje 12 kuma ya ce wa Jeroboam: ‘Jehobah zai ƙwace mulkin Isra’ila daga iyalin Sulemanu kuma zai raba shi waje biyu. Ka karɓi ƙyallaye goma na wannan rigar domin kai ne za ka yi mulki a kan ƙabilu goma na Isra’ila.’ Sa’ad da Sarki Sulemanu ya ji hakan, sai ya so ya kashe Jeroboam! Hakan ya sa Jeroboam ya gudu zuwa ƙasar Masar. Daga baya, sai Sulemanu ya mutu kuma ɗansa Rehoboam ya zama sarki. Da jin haka, sai Jeroboam ya dawo ƙasar Isra’ila.

Isra’ilawa suna bauta wa gunkin da Jeroboam ya yi

Dattawan Isra’ila suka ce wa Rehoboam: ‘Mutanen za su yi maka biyayya idan ka bi da su yadda ya dace.’ Amma sai wani abokin Rehoboam wanda shi matashi ne ya ce: ‘Ka ba mutanen wahala! Ka ba su aiki mai wuya!’ Rehoboam ya bi shawarar abokinsa. Ya taƙura wa mutanen kuma sun yi taurin kai. Sun naɗa Jeroboam sarkin ƙabilu goma kuma ƙabilun ne suka zama Isra’ila. Ƙabilu biyun kuma sun zama Yahudiya kuma sun ci gaba da yin biyayya ga Rehoboam. Haka aka raba ƙabilu 12 na Isra’ila waje biyu.

Urushalima yana yankin da Rehoboam yake mulki kuma Jeroboam ba ya so mutanensa su je bauta a wurin. Ka san dalilin? Domin Jeroboam yana tsoro cewa mutanen za su soma bin Rehoboam. Sai ya ƙera gunki guda biyu da suka yi kama da ƙananan shanu. Ya ce wa mutanen: ‘Urushalima tana da nisa sosai. Ku riƙa bauta a nan.’ Sai mutanen suka soma bauta wa gumakan kuma suka daina bauta wa Jehobah.

‘Kada ku yi [abota] marar dacewa da marasa ba da gaskiya. To, me ya haɗa aikin adalci da na mugunta? . . . Me kuma ya haɗa mai ba da gaskiya da marar ba da gaskiya?’​—2 Korintiyawa 6:​14, 15, Littafi Mai Tsarki

Tambayoyi: Me ya sa aka raba Isra’ila? Waɗanne zunubai ne Sarki Rehoboam da Jeroboam suka yi?

1 Sarakuna 11:​1-13, 26-43; 12:​1-33

    Littattafan Hausa (1987-2026)
    Fita
    Shiga Ciki
    • Hausa
    • Raba
    • Wadda ka fi so
    • Copyright © 2025 Watch Tower Bible and Tract Society of Pennsylvania
    • Ka'idojin Amfani
    • Tsarin Tsare Sirri
    • Saitin Tsare Sirri
    • JW.ORG
    • Shiga Ciki
    Raba