Watchtower LABURARE NA INTANE
Watchtower
LABURARE NA INTANE
Hausa
Ɓ
  • Ā
  • ā
  • Ɓ
  • ɓ
  • ɗ
  • Ɗ
  • Ƙ
  • ƙ
  • ꞌY
  • ꞌy
  • LITTAFI MAI TSARKI
  • WALLAFE-WALLAFE
  • TARO
  • w18 Oktoba p. 32
  • Ka Sani?

Babu bidiyo don wannan zabin

Yi hakuri, bidiyon na da dan matsala

  • Ka Sani?
  • Hasumiyar Tsaro Mai Shelar Mulkin Jehobah (Na Nazari)—2018
  • Makamantan Littattafai
  • An Jejjefi Istafanus
    Littafina na Labarun Littafi Mai Tsarki
  • Tambayoyi daga Masu Karatu
    Hasumiyar Tsaro Mai Shelar Mulkin Jehobah—2005
  • 3 | Ka Cire Kiyayya Daga Zuciyarka
    Hasumiyar Tsaro Mai Shelar Mulkin Jehobah (Na Wa’azi)—2022
  • Shan Tsanani Domin Adalci
    Hasumiyar Tsaro Mai Shelar Mulkin Jehobah—2003
Dubi Ƙari
Hasumiyar Tsaro Mai Shelar Mulkin Jehobah (Na Nazari)—2018
w18 Oktoba p. 32

Ka Sani?

Me ya taimaka wa Istifanus ya natsu sa’ad da ake tsananta masa?

Istifanus bai firgita ba sa’ad da yake gaban Majalisa

ISTIFANUS yana gaban mutane masu adawa da shi. Yana gaban Majalisa, wato kotu mafi girma a Isra’ila kuma alƙalai 71 mafi iko a al’ummar ne suke shari’ar. Babban Firist Kayafa ne ya tara su, kuma shi ne ya ja-goranci shari’a da aka yi wa Yesu ’yan watanni da suka shige kuma aka yanke wa Yesu hukuncin mutuwa. (Mat. 26:​57, 59; A. M. 6:​8-12) Mutane masu shaidar ƙarya suna zuwa ɗaya bayan ɗaya suna ba da shaida. Amma mutane da suke majalisar sun lura da wani abin ban-mamaki game da Istifanus. Sun ga cewa “fuskarsa ta zama kamar ta mala’ika.”​—A. M. 6:​13-15.

Me ya taimaka wa Istifanus ya natsu a irin wannan yanayin? Kafin a kai Istifanus gaban Majalisa yana hidimarsa da ƙwazo kuma ruhu mai tsarki ne yake taimaka masa. (A. M. 6:​3-7) Sa’ad da yake fuskantar wannan gwajin, ruhu mai tsarki yana tare da shi kuma ya taimaka masa. (Yoh. 14:16) Istifanus ya furta abin da ke rubuce a Ayyukan Manzanni sura 7 da gaba gaɗi sa’ad da yake kāre kansa. Kuma ruhu mai tsarki ya sa ya tuna abin da ke cikin ayoyi 20 ko kuma fiye da hakan a cikin Nassosin Ibrananci. (Yoh. 14:26) Ƙari ga haka, Istifanus ya sami ƙarfafa sosai sa’ad da ya ga wahayi game da Yesu yana tsaye a hannun dama na Allah.​—A. M. 7:​54-56, 59, 60.

Wata rana wataƙila mu ma za a yi mana barazana kuma a tsananta mana. (Yoh. 15:20) Amma ruhun Jehobah zai taimaka mana idan muna karanta Kalmar Allah a kai a kai kuma muna ƙwazo a hidima. Hakan zai sa mu sami ƙarfin jimre tsanantawa kuma mu natsu.​—1 Bit. 4:​12-14

    Littattafan Hausa (1987-2026)
    Fita
    Shiga Ciki
    • Hausa
    • Raba
    • Wadda ka fi so
    • Copyright © 2025 Watch Tower Bible and Tract Society of Pennsylvania
    • Ka'idojin Amfani
    • Tsarin Tsare Sirri
    • Saitin Tsare Sirri
    • JW.ORG
    • Shiga Ciki
    Raba