Watchtower LABURARE NA INTANE
Watchtower
LABURARE NA INTANE
Hausa
Ɓ
  • Ā
  • ā
  • Ɓ
  • ɓ
  • ɗ
  • Ɗ
  • Ƙ
  • ƙ
  • ꞌY
  • ꞌy
  • LITTAFI MAI TSARKI
  • WALLAFE-WALLAFE
  • TARO
  • lfb darasi na 10 p. 30
  • Ku Tuna da Matar Lutu

Babu bidiyo don wannan zabin

Yi hakuri, bidiyon na da dan matsala

  • Ku Tuna da Matar Lutu
  • Darussa daga Littafi Mai Tsarki
  • Makamantan Littattafai
  • Matar Lutu Ta Dubi Baya
    Littafina na Labarun Littafi Mai Tsarki
  • Allah Ya Ɗauki Alkawari da Ibrahim
    Littafi Mai Tsarki​—Wane Saƙo Ne Ke Cikinsa?
  • Ka Taimaka wa Mutane Su Jimre da Matsaloli
    Hasumiyar Tsaro Mai Shelar Mulkin Jehobah (Na Nazari)—2019
  • Ku Tuna da Matar Lutu
    Littafin Taro Don Rayuwa ta Kirista da Hidimarmu—2018
Darussa daga Littafi Mai Tsarki
lfb darasi na 10 p. 30
Matar Lutu ta zama tarin gishiri yayin da Lutu da kuma ’ya’yansa suka gudu suka bar Saduma

DARASI NA 10

Ku Tuna da Matar Lutu

Lutu ya zauna da kawunsa Ibrahim a ƙasar Kan’ana. Daga baya, sai Ibrahim da Lutu suka sami dabbobi da yawa kuma wurin da suke ya yi musu kaɗan. Ibrahim ya gaya wa Lutu cewa: ‘Ba zai yiwu mu ci gaba da zama tare ba. Don Allah a cikin wuraren nan, ka zaɓi wanda ka fi so.’ Ibrahim bai yi son kai ba, ko ba haka ba?

Lutu ya ga wani wuri mai kyau kusa da wani birnin da ake kira Saduma. Akwai ruwa da kuma ciyawa mai kyau da dabbobi za su ci. Sai ya zaɓi wurin kuma ya ƙaura da iyalinsa zuwa wurin.

Mutanen birnin Saduma da Gwamarata ba sa yin abu mai kyau. Jehobah ya ce zai halaka su don muguntarsu. Amma Jehobah ya aika mala’iku biyu don su ceci Lutu da iyalinsa. Sai mala’ikun suka ce: ‘Ka tashi! Ka fita daga birnin nan! Jehobah zai halaka shi.’

Lutu bai bar birnin da sauri ba. Yana ta ɓata lokaci. Sai mala’ikun suka riƙe hannayensa da na matarsa da kuma na yaransa, suka fitar da su daga birnin kuma suka gaya musu cewa: ‘Ku gudu! Kada ku kalli baya don ku tsira. Idan kuka juya, za ku mutu!’

An halaka Saduma da Gwamarata da wuta

Sa’ad da suka kai wani birni mai suna Zoar, sai Jehobah ya sa wuta ta halaka Saduma da Gwamarata. An halaka biranen nan gabaki ɗaya. Da matar Lutu ta ƙi yin biyayya kuma ta juya baya, sai ta zama tarin gishiri! Amma Lutu da yaransa sun tsira don sun yi biyayya ga Jehobah. Babu shakka, sun yi baƙin ciki don rashin biyayyar da ta yi. Amma sun yi murna don sun yi abin da Jehobah ya gaya musu.

“Ku tuna da matar Lutu.”​—Luka 17:32

Tambayoyi: Me ya sa Jehobah ya halaka Saduma da Gwamarata? Me ya sa matar Lutu ta zama tarin gishiri?

Farawa 13:​1-13; 19:​1-26; Luka 17:​28, 29, 32; 2 Bitrus 2:​6-9

    Littattafan Hausa (1987-2026)
    Fita
    Shiga Ciki
    • Hausa
    • Raba
    • Wadda ka fi so
    • Copyright © 2025 Watch Tower Bible and Tract Society of Pennsylvania
    • Ka'idojin Amfani
    • Tsarin Tsare Sirri
    • Saitin Tsare Sirri
    • JW.ORG
    • Shiga Ciki
    Raba