Watchtower LABURARE NA INTANE
Watchtower
LABURARE NA INTANE
Hausa
Ɓ
  • Ā
  • ā
  • Ɓ
  • ɓ
  • ɗ
  • Ɗ
  • Ƙ
  • ƙ
  • ꞌY
  • ꞌy
  • LITTAFI MAI TSARKI
  • WALLAFE-WALLAFE
  • TARO
  • lfb darasi na 23 p. 60-p. 61 par. 4
  • Sun Yi wa Jehobah Alkawari

Babu bidiyo don wannan zabin

Yi hakuri, bidiyon na da dan matsala

  • Sun Yi wa Jehobah Alkawari
  • Darussa daga Littafi Mai Tsarki
  • Makamantan Littattafai
  • Jehobah Ya Ba Da Dokokinsa
    Littafina na Labarun Littafi Mai Tsarki
  • Yadda Za Ka San Hanyoyin Jehobah
    Hasumiyar Tsaro Mai Shelar Mulkin Jehobah—2005
  • Ba Su Cika Alkawarinsu Ba
    Darussa daga Littafi Mai Tsarki
  • Bishiya Mai Cin Wuta
    Darussa daga Littafi Mai Tsarki
Dubi Ƙari
Darussa daga Littafi Mai Tsarki
lfb darasi na 23 p. 60-p. 61 par. 4
Isra’ilawa sun tsaya a gaban Dutsen Sinai

DARASI NA 23

Sun Yi wa Jehobah Alkawari

Isra’ilawa sun iso Dutsen Sinai kuma sun kafa tanti a wurin. Wajen wata biyu da barin ƙasar Masar, Jehobah ya gaya wa Musa ya hau dutsen. Bayan ya hau, sai Jehobah ya ce masa: ‘Na ceci Isra’ilawa kuma idan suka bi dokokina, za su zama mutanena na musamman.’ Sai Musa ya sauko kuma ya gaya wa Isra’ilawan abin da Jehobah ya gaya masa. Sai suka ce: ‘Za mu yi biyayya da duk wani abin da Jehobah ya ce mu yi.’

Sai Musa ya sake hau dutsen. Jehobah ya ce masa: ‘Nan da kwana uku, zan yi maka magana. Ka gaya wa mutanen kada su kuskura su hau Dutsen Sinai.’ Sai Musa ya sauka kuma ya gaya wa Isra’ilawa cewa su yi shiri don Jehobah yana son ya yi magana da su.

Isra’ilawa sun ga walkiya da kuma bakin gajimare a kan Dutsen Sinai

Bayan kwana uku, sai Isra’ilawa suka soma ganin walƙiya, kuma hadari ya rufe kan dutsen. Kuma suka ji tsawa da kuma ƙarar ƙaho. Sai Jehobah kewaye da wuta ya sauko kan dutsen. Isra’ilawan sun ji tsoro sosai har jikinsu ya soma rawa. Dutsen ya girgiza kuma hayaƙi ya rufe dutsen. Ƙarar ƙahon sai daɗa ƙaruwa take yi. Sai Allah ya ce: ‘Ni ne Jehobah kuma kada ku kuskura ku bauta wa wasu alloli.’

Sai Musa ya koma kan dutsen kuma Jehobah ya ba shi dokoki a kan abubuwan da mutanen za su riƙa yi da kuma yadda za su bauta masa. Musa ya rubuta dokokin kuma ya karanta wa Isra’ilawa. Mene ne Isra’ilawa suka ce? Sun yi alkawari cewa: ‘Za mu yi biyayya da duk wani abin da Jehobah ya ce mu yi.’ Sun yi wa Allah alkawari. Amma za su cika alkawarin kuwa?

“Ka ƙaunaci Ubangiji Allahnka da dukan zuciyarka, da dukan ranka, da dukan hankalinka.”​—Matta 22:​37, Littafi Mai Tsarki

Tambayoyi: Me ya faru a Dutsen Sinai? Wane alkawari ne Isra’ilawa suka yi?

Fitowa 19:1–20:21; 24:​1-8; Kubawar Shari’a 7:​6-9; Nehemiya 9:​13, 14

    Littattafan Hausa (1987-2026)
    Fita
    Shiga Ciki
    • Hausa
    • Raba
    • Wadda ka fi so
    • Copyright © 2025 Watch Tower Bible and Tract Society of Pennsylvania
    • Ka'idojin Amfani
    • Tsarin Tsare Sirri
    • Saitin Tsare Sirri
    • JW.ORG
    • Shiga Ciki
    Raba