Ka Koya Daga Kalmar Allah
Me Ya Sa Allah Yake da Ƙungiya?
Wannan talifin ya tattauna tambayoyin da wataƙila ka taɓa yin tunani a kansu kuma ya nuna inda za ka iya samun amsoshinsu a cikin naka Littafi Mai Tsarki. Shaidun Jehobah za su yi farin cikin tattauna waɗannan amsoshin da kai.
1. Me ya sa Allah ya tsara Isra’ilawa?
Allah ya kafa zuriyar Ibrahim ta zama al’umma kuma ya ba ta dokokin da za ta bi. Ya kira al’ummar, Isra’ila, kuma ya ɗora mata nauyin kāre bauta ta gaskiya da kuma Kalmarsa, Nassosi Masu Tsarki. (Zabura 147:19, 20) Hakan ya sa mutane daga dukan al’umma suka amfana.—Karanta Farawa 22:18.
Allah ya zaɓi Isra’ilawa su zama shaidunsa. Sa’ad da suka yi biyayya, sun amfana daga dokokin Allah. (Kubawar Shari’a 4:6) Yin nazarin tarihin Isra’ilawa zai taimaka mana mu ƙara sanin Allah na gaskiya.—Karanta Ishaya 43:10, 12.
2. Me ya sa Kiristoci na gaskiya suke da tsari?
Bayan wani lokaci, Isra’ila ta juya wa Allah baya, kuma Jehobah ya sauya al’ummar da ikilisiyar Kirista. (Matta 21:43; 23:37, 38) A dā, Isra’ilawa shaidun Allah ne. Amma, yanzu Kiristoci na gaskiya ne suka zama shaidun Jehobah.—Karanta Ayyukan Manzanni 15:14, 17.
Yesu ya koya wa mabiyansa su riƙa yin aiki a matsayin rukuni wajen yin wa’azi game da Jehobah da kuma yin almajirai a dukan al’ummai. (Matta 10:7, 11; 24:14; 28:19, 20) Wannan aikin yana gab da ƙarewa. Wannan shi ne lokaci na farko da Jehobah ya haɗa kan miliyoyin mutane daga dukan ƙasashen duniya a bauta ta gaskiya. (Ru’ya ta Yohanna 7:9, 10) An umurce Kiristoci na gaskiya su riƙa yin aiki tare a matsayin rukuni don su ƙarfafa juna su kuma taimaki juna. A faɗin duniya, suna bin tsari guda wajen koyar da umurnin da ke cikin Littafi Mai Tsarki a taronsu.—Karanta Ibraniyawa 10:24, 25.
3. Ta yaya aka kafa ƙungiyar Shaidun Jehobah a wannan zamanin?
Wani ƙaramin rukunin ɗaliban Littafi Mai Tsarki sun soma gano gaskiyar da ke cikin Littafi Mai Tsarki wadda ta ɓace tun da daɗewa. Sun san cewa Yesu ya umurci waɗanda ke cikin ikilisiyar Kirista su yi wa’azi. Hakan ya sa suka soma wa’azin Mulki a dukan ƙasashen duniya. Sun soma amsa sunan nan Shaidun Jehobah ne a shekara ta 1931.—Karanta Ayyukan Manzanni 1:8; 2:1, 4; 5:42.
4. Yaya aka tsara Ƙungiyar Shaidun Jehobah a yau?
A ƙarni na farko, ikilisiyoyin Kirista a ƙasashe da dama sun amfana daga Hukumar Mulki da ke Urushalima wadda ta ɗauki Yesu a matsayin Shugaban ikilisiya. (Ayyukan Manzanni 16:4, 5) Hakazalika a yau, Shaidun Jehobah sun ɗauki Yesu a matsayin Shugabansu. (Matta 23:9, 10) Suna kuma amfana daga ja-gorancin Hukumar Mulki wadda ta ƙunshi ƙwararrun dattawa waɗanda suke tanadar da ƙarfafawa da kuma ja-gora daga Nassi ga ikilisiyoyi fiye da 100,000. A kowace ikilisiya, maza da suka cancanta suna hidima a matsayin dattawa ko masu kula. Waɗannan mazajen suna kula da tumakin Allah cikin ƙauna.—Karanta 1 Bitrus 5:2, 3.
Shaidun Jehobah suna yin wa’azi da kuma almajirantarwa. Don su taimaka wa mutane a ko’ina, suna fassara da kuma buga littattafan da ke bayyana Littafi Mai Tsarki a cikin harsuna fiye da 500, sa’an nan su rarraba su. Kamar manzannin Yesu, suna wa’azi gida-gida. (Ayyukan Manzanni 20:20) Suna yin nazarin Littafi Mai Tsarki da mutanen da ke son su koyi gaskiya. Tun da yake mutanen Jehobah sun mai da hankali ne ga faranta wa Allah rai da kuma taimaka wa mutane, su ƙungiya ce ta mutane masu farin ciki.—Karanta Zabura 33:12; Ayyukan Manzanni 20:35.
Domin ƙarin bayani, ka duba babi na 19 na wannan littafin, Menene Ainihi Littafi Mai Tsarki Yake Koyarwa?, Shaidun Jehobah ne suka wallafa.