Watchtower LABURARE NA INTANE
Watchtower
LABURARE NA INTANE
Hausa
Ɓ
  • Ā
  • ā
  • Ɓ
  • ɓ
  • ɗ
  • Ɗ
  • Ƙ
  • ƙ
  • ꞌY
  • ꞌy
  • LITTAFI MAI TSARKI
  • WALLAFE-WALLAFE
  • TARO
  • w14 11/1 pp. 8-9
  • Mulkin Allah​—⁠Ta Yaya Zai Amfane Ka?

Babu bidiyo don wannan zabin

Yi hakuri, bidiyon na da dan matsala

  • Mulkin Allah​—⁠Ta Yaya Zai Amfane Ka?
  • Hasumiyar Tsaro Mai Shelar Mulkin Jehobah—2014
  • Makamantan Littattafai
  • Mulkin Allah​—⁠Me Ya Sa Yake da Muhimmanci ga Yesu?
    Hasumiyar Tsaro Mai Shelar Mulkin Jehobah—2014
  • Amsoshin Tambayoyi Daga Littafi Mai Tsarki
    Hasumiyar Tsaro Mai Shelar Mulkin Jehobah—2014
  • Ka Goyi Bayan Mulkin Allah Yanzu!
    Hasumiyar Tsaro Mai Shelar Mulkin Jehobah (Na Wa’azi)—2020
  • Abin da Yesu Ya Koyar Game da Mulkin Allah
    Hasumiyar Tsaro Mai Shelar Mulkin Jehobah—2010
Dubi Ƙari
Hasumiyar Tsaro Mai Shelar Mulkin Jehobah—2014
w14 11/1 pp. 8-9

ABIN DA KE SHAFIN FARKO | MULKIN ALLAH​—TA YAYA ZAI AMFANE KA?

MULKIN ALLAH ​—Ta Yaya Zai Amfane Ka?

Mai yiwuwa daga bayanan da aka yi a talifofin baya, ka fahimci cewa Shaidun Jehobah suna ɗaukan Mulkin Allah da muhimmanci sosai. Wataƙila wasu daga cikin albarkun da aka bayyana cewa Mulkin Allah zai kawo nan gaba sun burge ka. Amma, kana iya ganin kamar da wuya waɗannan alkawuran su cika.

A gaskiya, maimakon ka gaskata da duk abin da ka ji haka kawai, zai dace ka yi hattara. (Misalai 14:15) Akwai wasu mutane a birnin Biriyaa ta dā da suka yi hattara kamarka. Sa’ad da suka ji bisharar Mulkin, sun ba da gaskiya, amma ba don sun so su yi hakan kawai ba. Maimakon haka, sun bincika Nassosi da kyau don “su gani ko waɗannan al’amura haka suke.” (Ayyukan Manzanni 17:11) Mutanen Biriya sun gwada bisharar da suka ji da abin da ke cikin Littafi Mai Tsarki. A sakamakon haka, sun gaskata cewa bisharar daga Kalmar Allah ce.

Shaidun Jehobah suna ƙarfafa ka ka yi hakan kai ma. Nazarin Littafi Mai Tsarki da muke yi da mutane kyauta zai ba ka damar gwada abubuwan da Shaidun Jehobah suka gaskata game da Mulkin Allah da kuma koyarwar Littafi Mai Tsarki.

Ban da haka ma, yin nazarin Littafi Mai Tsarki zai taimaka maka ka sami amsoshin tambayoyi masu muhimmanci game da rayuwa, kamar waɗanda ke gaba.

  • Ta yaya muka soma wanzuwa?

  • Mece ce manufar rayuwa?

  • Me ya sa Allah ya ƙyale mutane su sha wahala?

  • Me ke faruwa da mutum bayan ya mutu?

  • Za a hallaka duniya ne?

  • Me zai taimaka wa iyali ta zauna lafiya?

Mafi muhimmanci shi ne, yin nazarin Littafi Mai Tsarki zai taimaka maka ka “kusato ga Allah.” (Yaƙub 4:8) Yayin da kake daɗa kusantar Allah, za ka ga yadda Mulkin Allah zai amfane ka a yanzu da kuma har abada. Yesu da kansa ma ya ambata cikin addu’a ga Ubansa cewa: ‘Rai na har abada ke nan, su san ka, Allah makaɗaici mai-gaskiya, da shi kuma wanda ka aiko, Yesu Kristi.’—Yohanna 17:3.

Shaidun Jehobah za su iya yin nazarin Littafi Mai Tsarki da kai ta wannan littafin.

Idan kana so a yi nazarin Littafi Mai Tsarki da kai kyauta, ka sami ɗaya daga cikin Shaidun Jehobah ko kuma ka cika wani fom a dandalin www.pr418.com/ha. (Ka duba inda aka rubuta IN KANA SO A YI NAZARIN LITTAFI MAI TSARKI DA KAI a shafin farko na dandalinmu)

a Biriya wani birni ne a ƙasar Makidoniya ta dā.

Abin da Ya Sa Take Son Mulkin Allah

A kwana kwanan nan, an sa wata ’yar makaranta ’yar shekara goma mai suna Folake ta yi rubutu a kan jigon nan, “Abin da Na Fi So a Wannan Duniya.” Folake ta zaɓi ta yi rubutu a kan dalilin da ya sa take son gaya wa mutane game da Mulkin Allah.

Folake ta yi bayani cewa “Mulkin Allah gwamnati ce ta zahiri.” Ta daɗa da cewa “Amma mutum ba zai iya ganinsa ba, ko da ya saka gilashi!”

Sai Folake ta yi rubutu a kan albarkun Mulkin da take ɗokin morewa. Sa’ad da take ambata wasu matsalolin da Mulkin zai magance, ta ce: “Ina baƙin ciki sa’ad da na ga mutane suna kwana a kan titi domin ba su da gidaje” da kuma “ƙananan yara da suke mutuwa saboda yunwa a wurare dabam-dabam a duniya.” Ta ƙara da cewa: “Amma ina farin ciki sa’ad da na karanta Ishaya 65:21.” Ayar ta nuna cewa mutanen da za su zauna a cikin Mulkin Allah “za su gina gidaje, kuma za su zauna a ciki; su yi gonakin anab kuma, su ci amfaninsu.”

Ƙari ga haka, Folake ta ce tana sa zuciyar ganin lokacin da Allah zai kawar da kowane irin cuta ta wurin Mulkinsa. A cikin rubutunta, ta yi ƙaulin Ru’ya ta Yohanna 21:4, wadda ta ce Allah “zai share dukan hawaye kuma daga idanunsu: mutuwa kuwa ba za ta ƙara kasancewa ba; ba kuwa za a ƙara yin baƙin ciki, ko kuka, ko azaba” ba. Sa’ad da take kammala rubutunta, ta sake rubuta cewa yin wa’azi game da Jehobah da kuma Mulkinsa ne abin da ta fi so a wannan duniyar. Hakika, wannan ƙaramar yarinyar tana son Mulkin Allah sosai!

    Littattafan Hausa (1987-2026)
    Fita
    Shiga Ciki
    • Hausa
    • Raba
    • Wadda ka fi so
    • Copyright © 2025 Watch Tower Bible and Tract Society of Pennsylvania
    • Ka'idojin Amfani
    • Tsarin Tsare Sirri
    • Saitin Tsare Sirri
    • JW.ORG
    • Shiga Ciki
    Raba